Duk wanda Allah ya azurta shi, da samun abu biyar, a rayuwarsa, yayi babban arziki.
Na daya: biyayyya ga umarnin Allah, idan yace ayi to ka tashi kayi, iyawarka, domin Allah kuma akan sunnah.
Na biyu, : idan Allah yayi hani ka hanu, domin hanuwar shine arzikin ka duniya da lahira,
Na uku,: Idan Allah ya baka kayi godiya, da gabbanka da zuciyrka da bakinka, kuma ka aiwatar da ita ta hanyar da ta dace,
Na hudu,: Idan Allah ya jarrabeka kayi hakuri, ka mayar da komai ga Allah,
Na biyar,: Idan kayi laifi, ka tuba, kayi nadama da istigfari.
Allah yasa mu dace.
BABBAN ARZIKI !
Tags:
Addini

0 comments: